in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar sojin ruwan Najeriya ta karbi jirgin ruwan sintiri kirar kasar Sin
2015-02-07 16:53:31 cri
Kamfanin kirar jiragen ruwan kasar Sin na CSOC, ya mikawa rundunar sojin ruwan tarayyar Najeriya wani sabon jirgin ruwan sintiri da ya kera, a wani mataki na tallafawa yaki da laifukan da suka jibanci ruwayen kasar, da ma na gabar tekun guinea.

Kazalika ana fatan gabatarwa Najeriyar karin wani jirgin sintirin nan gaba cikin wannan shekara.

Da yake karbar jirgin a madadin rundunar sojin ruwan Najeriya,Vice Admiral Usman Jibrin, ya ce jirgin zai yi matukar tallafawa sojin ruwan kasa, a fannin yaki da laifukan da suka jibanci ruwan kasar.

Jibrin ya kara da cewa akwai dadaddiyar alaka tsakanin kasar Sin da Najeriya, a fannin samarwa Najeriyar jiragen yakin ruwa.

A nasa tsokaci, karamin jakadan Sin a Najeriya Liu Kan, cewa ya yi kasar sa za ta ci gaba da inganta kyakkyawar alakar dake tsakanin ta da Najeriya.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China