in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalissar zartarwar Nigeriya zata gana kafin babban zaben kasar
2015-02-04 20:34:11 cri
Ana sa ran Majalissar zartarwar Nigeriya zata gana a ranar alhamis din nan a Abuja babban birnin tarayyar Nigeriya domin tattauna kiran da ake yin a dage babban zaben kasar dake tafe a wannan watan da sauran batutuwa da suka shafi kasar.

Ganawar da ake sa ran Shugaba Goodluck Jonathan zai shugabanta zai kuma duba shirye shiryen da hukumar zabe mai zaman kanta ta yi a kan babban zaben da kuma na bangaren tsaro.

Wadansu daga cikin matsalolin dake kunno kai na zaben shi ne rashin kammala rarraba katunan zabe ga jama'a da hukumar zabe tayi, sai dai hukumar zaben a nata bangaren tace babu gudu babu ja da baya a game da ranar da ta tsaida na zabukan kasar.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China