Jami'iyyar ta cimma wannan matsaya ne sakamakon rahoton da kwamitin da ta kafa akan fidda dan takara, inji kakakin jam'iyar Abdul Isiaq a Abuja babban birnin kasar.
Babban shugaban jam'iyyar Olu Falae ya nuna alamun gazawar jam'iyar na tsaida dan takarar shugaban kasa wanda ya sa aka cimma wannan matsaya.
Abdul Isiaq yace kwamitin, a cikin rahotonsa ga shuagaban jam'iyyar ta yanke shawarar hakan ne ganin cewa dukkan sauran 'yan takarar jami'yyun kasa babu wanda ya nemi goyon bayanta in banda Shugaban Nigeriya mai ci yanzu Goodluck Jonathan.
Yace kwamitin ya lura cewa PDP ta amince da sharuddan da jami'iyar ta SDP ta gabatar idan har ana son goyon bayanta.