in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
CCDI ya bukaci goyon bayan jama'a wajen yaki da cin hanci
2015-01-14 20:11:22 cri
Kwamitin ladabtarwa na JKS ya bukacin jama'a da su ba tasu gudumawa a kokarin da ake na yaki da cin hanci da rashawa.

Kwamitin wanda ya bayyana haka cikin wata sanarwar da aka ba da a karshen cikakken zama na 5 na kwamitin ladabtarwa na JKS karo na 18 da ya gudana daga ranakun Litinin zuwa Laraba a nan birnin Beijing, ya kuma bayyana cewa, akwai bukatar a dauki matakai na siyasa, da nuna juriya wajen kawar da wannan matsala.

Bugu da kari sanarwar ta ce, muddin ana bukatar a kawar da matsalar cin hanci, akwai bukatar jama'a su ba da goyon baya tare da shiga a dama da su sosai har ma da kafofin watsa labarai.

Sanarwar ta kuma yi kira ga dukkan kwamitoci na JKS a dukkan matakai da su kara daura damara a wannan yaki.

A shekarar da ta gabata ce aka sake nazarin aikin da ake kan yaki da cin hanci inda aka bayyana cewa, an cimma nasarori da dama a karkashin shugabancin JKS, kokarin dukkan hukumomi da mambobin jam'iyya gami da goyon bayan jama'a da kuma aikin tukuru na sipetocin ladabtarwa. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China