in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin ya binciki ayyukan gyare-gyaren tsoffin gidaje masu hadari
2015-01-06 16:42:00 cri
A Talatar nan ne firaministan kasar Sin Li Keqiang ya ziyarci gundumar Baiyun a birnin Guangzhou dake kudancin kasar Sin, domin gudanar da bincike kan ayyukan gyare-gyare ga tsoffin gidaje masu hadari.

A yayin ziyarar aikin, firaminista Li ya ce ana kokarin neman bunkasuwa ba tare da la'akari da bambance-bambance ba, bisa wannan buri ya zama dole a kyautata yanayin rayuwar ma'aikata 'yan cin rani, da na masu fama da talauci a birane. Kana a samar da wani muhallin kasuwanci, da zai bude kofar takara cikin daidaito, da kwazo na samar da hidima ta zaman daidai wa daida ga jama'a, ta yadda za su iya karfafa fatansu game da rayuwarsu a nan gaba.

Firaminista Li ya nanata tambaya ga mazauna yankin game da ra'ayinsu kan gyare-gyaren tsoffin gidaje masu hadari. Bayan kuma samun amincewarsu, Mr. Li ya bayyana cewa kamata ya yi gwamnatin yankin ta gaggauta gudanar da wannan aiki domin biyan bukatun jama'a, yana mai fatan cewa, mazauna wurin za su kasance cikin sabbin gidajensu, a yayin ziyararsa ta nan gaba. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China