in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya bukaci dukkan bangarori a Gambia da su kai zuciya nesa
2015-01-01 16:38:20 cri
Babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya yi kira ga dukkan bangarorin da ke kasar Gambia da su kai zuciya nesa tare da kaucewa kara rura wutar tashin hankali.

Ban ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa ta hannun kakakinsa, inda ya bukaci da a gudanar da bincike na musamman dangane da yankurin juyin mulkin da wasu sojoji suka yi a kasar ranar 30 ga watan Disamba da bai yi nasara ba.

Sanarwar ta kuma yi kira ga gwamnatin kasar ta Gambia da dakarunta na tsaro da su gudanar da ayyukansu bisa la'akari da kare hakkin bil-adama. Ya kuma nanata akidar MDD na yin allawadai da duk wani yukurin kwace mulki ta hanyar da ta sabawa doka.

A ranar Talata ce aka yi yunkurin kifar da gwamnatin Yahya Jammeh na Gambia, bayan da aka rika jin harbe-harbe a Banjul, babban binrin kasar, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar wasu sojoji 5 baya ga wasu da dama aka kama.

Rahotanni na cewa, yanzu dai shugaba Jammeh ya dawo kasar bayan wani bulagura da ya yi tare da iyalansa zuwa Dubai a makon da ya gabata. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China