Cikin wata sanarwar da kakakinsa ya fitar, Mr. Ban ya mika sakon ta'aziyyarsa ga gwamnatin kasar Sin, da kuma iyalan wadanda bala'in ya rutsa da su, yana mai fatan wadanda suka jikkata za su murmure cikin sauri.
Ya ce MDD a shirye take ta tallafi duk wani shiri na bada tallafin jin kai, da samar da taimakon kasa da kasa a duk lokacin da bukatar hakan ta bijiro. (Saminu Hassan)