in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Magatakardan MDD ya nada babban jami'i na shirin bunkasa Afirka
2013-07-17 10:09:38 cri
A ranar Talata Magatakardan MDD Ban Ki-Moon ya sanar da nada Abdoulaye Mar Dieye na kasar Senegal a matsayin mataimakin mai gudanarwa kuma darektan ofishin yanki na shirin bunkasa na MDD wato (UNDP) a nahiyar Afirka.

Dieye zai maye gurbin Tegegnework Gettu wanda shi ma ya kama sabon aikinsa a matsayin mataimakin sakatare janar kan babban taro da gudanar da tarukan MDD, in ji sanarwar.

Dieye ya hau wannan mukami ne dauke da dimbin nasarori da ya cimma a baya a karkashin shirin na UNDP, wadanda suka hada da kasancewa kan mukamin shugaban ma'aikata da kuma darektan ofishin zartaswa.

Kafin a nada shi kan wannan matsayi, Dieye ya hau mukamin mataimakin darektan yanki, a yankin kasashen larabawa, da birnin New York, da kula da shirye-shiryen UNDP a arewacin Afirka, yankin gabas ta tsakiya da kuma na kasashen yankin Gulf. (Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China