in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
IGAD ta yi taro akan rikicin Sudan ta kudu
2014-11-07 17:12:13 cri
An yi taro na musamman karo na 28 na shugabannin kungiyar neman ci gaba ta tsakanin gwamnatocin gabashin Afrika IGAD a ranar alhamis din nan game da rikicin kasar Sudan ta kudu.

Kungiyar tana shiga tsakani ne don samar da zaman lafiya a kasar ta Sudan ta kudu.

Duk da cewar bangarorin biyu dake gaba da juna sun rattaba hannu akan yarjejeniya a gaban masu shiga tsakani na IGAD, saba alkawurra na ta kunno kai na ganin rikicin ya cigaba da wanzuwa. Firaministan kasar Habasha Hailemariam Desalegn wanda shi ne shugaban kungiyar ta IGAD a wajen bude taron ya ce duk da yarjejeniyar da aka cimma na kawo karshen rikicin a kuma fara shirin da zai kafa gwamnati sahihiya da za ta kawo karshen tashin hankali a kasar, wadannan alkawurra an lura ana aiwatar da sabanin hakan.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China