in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane a kalla 60 sun mutu a sakamakon fashewar boma-bomai a Nijeriya
2014-11-26 10:42:17 cri
Wasu hare haren boma-bomai guda biyu da aka kaddamar a wata kasuwa dake birnin Maidugurin jihar Borno a arewa maso gabashin tarayyar Nijeriya, sun sabbaba mutuwar mutane a kalla 60, tare da jikkata wasu fiye da 10.

Bisa labarin da gidan telebijin na Al Jazeera na kasar Qatar ya bayar, an ce boma-boman sun fashe ne a jiya Talata da misalin karfe 11 na rana bisa lokacin wurin, bayan da wata mace ta tashi bam din dake jikinta cikin dandazon jama'a. Jim kadan da hakan ne kuma wata macen daban ita ma ta tarwatsa kanta, a kusa da inda bam din na farko ya tashi.

Sai dai majiyar kamfanin dillancin labaru ta AFP ta ce mutane 45 ne harin bom din ya hallaka.

Bayan aukuwar hare-haren biyu an ga motocin jami'an bada agajin gaggawa na garzayawa wurin da lamarin ya auku. Inda suka rika kai mutanen da suka ji raunika zuwa asibitin dake kusa da wurin, yayin da dakarun rundunar soji ke kula da asibitin.

Wani da ya shaida yadda lamarin ya auku, ya ce akwai matukar cunkoson marasa lafiya a asibitin, sakamakon yawan wadanda suka jikkata a wannan lamari.

Ya zuwa yanzu dai babu wata kungiyar da ta dauki alhakin kaddamr da hare-haren. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China