in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
WFP ta gode da taimakon da kasar Sin ta bayar wajen yakar cutar Ebola
2014-11-19 20:15:38 cri
A jiya Talata 18 ga wata ne, hukumar samar da abinci ta MDD, wato WFP ta bayyana cewa, a lokacin da ake cikin mawuyacin hali na kokarin hana kara yaduwar cutar Ebola, ba ma kawai kasar Sin ta samar da abinci ga hukumar ba, har ma ta tura likitoci da ma'aikatan kiwon lafiya da kayayyakin asibiti zuwa yankuna masu fama da cutar. Sabo da haka, hukumar tana nuna godiya ga taimakon da gwamnatin kasar Sin ta bayar cikin lokaci ba tare da son kai ba.

Hukumar WFP ta bayyana cewa, annobar Ebola ba matsala ce ta wata kasa kawai ba, babban kalubale ne da ya shafi kasashen duniya baki daya. Ya zuwa yanzu, gamayyar kasa da kasa ta riga ta samu ci gaba wajen biyan bukatun jama'an da suke fama da cutar. Kasar Sin ta riga sauran kasashen duniya wajen daukar matakan bayar da taimako. Daga lokacin da aka samu barkewar cutar, gwamnatin kasar Sin ta samar wa kasashen yammacin Afirka da ke fama da cutar taimakon jin kai da darajarsa ta kai kudin Sin RMB yuan miliyan 750, wannan ya alamta cewa, kasar Sin tana cika alkawarin da ta yi wa duniya wajen samar da kayayyakin jin kai, a duk lokacin da bukatar hakan ta taso. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China