in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNICEF za ta kara yawan ma'aikatanta a kasashen yammacin Afirka don taimakawa wajen yaki da cutar Ebola
2014-11-04 15:57:24 cri
Jami'in asusun tallafawa yara na MDD UNICEF kan cutar Ebola Peter Salama ya bayyana a ranar 3 ga wata cewa, a sakamakon yadda cutar ta yi mummanan tasiri ga kananan yara a kasashen yammacin Afirka masu fama da cutar Ebola, asusun zai kara yawan ma'aikatansa a kasashen daga 300 zuwa 600 don taimaka musu wajen yaki da cutar Ebola.

Salama ya bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar a cibiyar MDD dake birnin New York a wannan rana cewa, asusun zai kuma taimaka wajen tsugunar da yara marayu kimanin 4000 da suka rasa iyayensu sakamakon cutar ta Ebola. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China