in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara yin jigilar kayayyakin taimakon rigakafi da yaki da cutar Ebola zagaye na uku na kasar Sin
2014-10-27 11:00:15 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin cinikayya ta kasar Sin Sun Jiwen ya bayyana a yau Litinin 27 ga wata a nan birnin Beijing cewa, an fara yin jigilar kayayyakin taimakon rigakafi da yaki da cutar Ebola zagaye na uku da kasar Sin ta yi alkawarin bayarwa da darajarsu ta kai kudin Sin Yuan miliyan 200, inda ake sa ran cewa, za su isa wasu kasashen Afirka bi da bi kafin ranar 31 ga wata don fara yin amfani da su cikin hanzari.

Sun Jiwen ya yi jawabi kan halin da ake ciki dangane da matakan samar da kayayyakin taimakon rigakafi da yaki da cutar Ebola zagaye na uku ga kasashen Afirka da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sanar. Sun ya bayyana cewa, a halin yanzu, jiragen saman da za su yi dakon kayayyakin da kasar Sin ta bayar sun tashi da karfe 3 da minti 12 na safiyar yau Litinin daga filin jirgin saman birnin Tianjin zuwa kasashe shida na Afirka ciki har da kasar Mali, kuma jirgin saman da zai je kasar Nijeriya ya riga ya tashi daga birnin Beijing. Kayayyakin da za a yi jigilarsu a wannan karo sun hada da rigunan kafiya, tabarau na kariya, na'urorin binciken zafin jiki da dai sauransu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China