in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 4922 sun mutu a sakamakon kamuwa da cutar Ebola a duniya
2014-10-26 17:00:08 cri
Bisa alkaluman da kungiyar hukumar kiwon lafiya ta duniya,( WHO) ta gabatar, an ce, tun daga watan Maris na bana da cutar Ebola ta barke, baki daya mutane sama da dubu 10 sun kamu da cutar Ebola, a ciki mutane 4922 sun mutu a sakamakon haka.

An nuna cewa, kKasashen Guinea da Saliyo da Liberia dake yammacin nahiyar Afirka sun fi fama da cutar Ebola, kuma mafi yawan mutanen da suka mutu sakamakon kamuwa da cutar Ebola sun fito daga wadannan kasashe uku.

Bisa wani labari mai dumi dumi da aka bayar, an ce, yarinyar da aka tabbatar da kamuwa da cutar Ebola ta farko a Mali ta rasu. Kuma tuni gwamnatin kasar Mali ta shelanta cewa, yarinyar tare da iyalinta sun dawo daga wata ziyara a kasar Guinea. Yanzu an riga an kebe mutane sama da 40 da suka taba mu'amala da wannan yarinya zuwa wani wuri na daban.

Kungiyar WHO ta yi gargadi cewa, mai yiyuwa ne yawan mutanen da suka kamu da cutar Ebola ya zai kara karuwa a nan gaba.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China