in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Zambiya ya zargi hannun kasashen Turai a cikin yake yaken Afrika
2014-04-05 16:19:44 cri
Shugaban kasar Zimbiya Micheal Sata ya zargi kasashen Turai da iza wutar tashe tashen hankali a nahiyar Afrika.

A yayin taron Afrika da Tarayyar Turai da aka kammala a birnin Bruxells, shugaban Zambiya ya kuma zargi kasashen yammacin duniya da gudanar da manufar bita da kulli tare da nahiyar Afrika.

Shugaban mai shekaru 76 a duniya ya fada wa kasashen Turai cewa Afrika bata da kamfanonin dake kera makamai don kara rura wutar yake yake, kana kasashen Turai ne ke bayan wadannan yake yake a nahiyar Afrika domin makaman da ake yaki da su kirar kasashen Turai ne.

A cewarsa yawancin kananan yaran da ake gani cikin yake yake a Afrika suna dauke da makaman da ake kera daga Turai da suka shafi miliyoyin dalar Amurka, tare da kara da cewa in ba haka ba ina wadannan yara matalauta zasu samu kudin sayen wadannan makamai.

Haka kuma mista Sata ya bayyana cewa gwamnatinsa tana maida hankali kan tsarin mulki nagari da ya kasance babban matakin samun cigaba da wadata. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China