in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gudanar da bikin taya murnar cika shekaru 65 da kafa sabuwar kasar Sin a kasar Zimbabwe
2014-09-26 10:37:04 cri
An gudanar da bikin taya murnar cika shekaru 65 da kafa sabuwar kasar Sin a ofishin jakadancin Sin dake kasar Zimbabwe a ranar Alhamis 25 ga wata, inda manyan jami'an kasar Zimbabwe, da jami'an diplomasiya na kasa da kasa, wakilan hukumomin Sin dake kasar Zimbabwe, da al'ummar Sinawa dake kasar suka halarta.

Jakadan Sin a kasar Zimbabwe Lin Lin ya bayyana a cikin jawabinsa cewa, kasar Sin za ta ci gaba da bude kofa ga kasashen ketare da yin kwaskwarima a gida, da bunkasa kasa cikin lumana, kana za ta kara bayyana ra'ayoyin kasashe masu tasowa da kuma taimake su wajen neman moriyar kansu a harkokin duniya. Jakadan kuma ya jaddada cewa, kasar Sin ta dora muhimmanci sosai kan dangantakar dake tsakaninta da kasashen Afirka, an samu nasarori da kyakkyawan sakamako kan ziyarar shugaban kasar Sin Xi Jinping a kasashen Afirka a bara, bisa wannan tushe Sin za ta kara yin hadin gwiwa a tsakanin sassan biyu a dukkan fannoni bisa ka'idojin nuna gaskiya na hakika, da sada zumunta.

A daya hannun kuma jakadan ya bayyana cewar bayan da cutar Ebola ta bullo, kasar Sin ta tura masu aikin jinya zuwa kasashe masu fama da cutar nan take don taimaka masu wajen yaki da cutar, abin da ya bayyana kyakkyawar zumunta a tsakanin Sin da kasashen Afirka. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China