in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya halarci taron koli na kungiyar SCO a Tajikistan
2014-09-12 15:27:22 cri
Yau Jumma'a 12 ga wata, an yi taron karo na 14 na majalisar shugabannin kasashe membobin kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai (SCO) karo na 14 a birnin Dushanbe, hedkwatar Tajikistan. Shugaban kasar Sin Xi Jinping da sauransu sun halarci wannan taro, inda kuma shugaba Xi zai yi wani muhimmin jawabi.

Wani jami'in ma'aikatar harkokin waje ta Sin ya bayyana cewa, a cikin yayin taron kolin, za a yi shawarwari kan muhimman batutuwa biyar. Wato, na farko, yin shawarwari kan kara kyautata ayyukan kungiyar SCO, da kiyaye zaman lafiya a shiyya-shiyya, da sa kaimi ga hadin gwiwa tsakaninsu a fannin tattalin arziki. Na biyu, yin musayar ra'ayi kan manyan harkokin duniya da na shiyya-shiyya. Na uku, kyautata hadin gwiwa tsakanin kasashe masu sa ido na kungiyar SCO da kasashe masu yin shawarwari da su. Na hudu, tabbatar da kasar da za ta ba da jagoranci a kungiyar SCO daga shekarar 2014 zuwa ta 2015. Na biyar, sa hannu da kuma gabatar bayar da sanarwar Dushanbe.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China