in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta nuna rashin amincewa da ganawar da Obama zai yi da Dalai Lama
2014-02-21 14:29:45 cri
A Jumma'a ranar 21 ga wata, kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin, Madam Hua Chunying ta bayyana cewa, Sin na mai da hankali sosai kan ganawar da shugaban kasar Amurka, Barack Obama zai yi tare da Dalai Lama, kuma ta bayyana wa Amurka rashin jin dadinta dangane da batun.

Kakakin ta yi nuni da cewa, harkar da ta shafi Tibet harkar cikin gida ce ta kasar Sin, wadda bai kamata ba wata kasar waje ta tsoma baki a ciki. Dalai Lama ya dade yana yunkurin neman jawo baraka ga kasar Sin inda yake fake da addini. Don haka, ganawar da shugaban kasar Amurka zai yi da Dalai Lama tamkar tsoma baki ne a cikin harkokin gida na kasar Sin, wadda za ta keta ka'idar da ta shafi huldar da ke tsakanin kasa da kasa, wadda kuma za ta iya lalata huldar da ke tsakanin Sin da Amurka. Don haka, kasar Sin na nuna matukar rashin amincewarta.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China