in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar EU tana shirin ci gaba da daukar karin matakai kan Rasha
2014-08-31 17:24:56 cri
An kammala taron musamman, na shugabanni kungiyar tarayyar kasashen Turai ta EU a daren jiya Asabar, tare da tsaida kudurin gabatar da wasu shawarwari cikin makon dake tafe. Shawarwarin da ake sa ran za su zamo tamkar share fage ga ci gaba da daukar karin matakai kan kasar Rasha.

Wasu takardun bayan taron da aka fitar sun bayyana bukatar da majalisar kasashen Turai ta gabatar ga kwamitin kungiyar EU game da kara kwazo, ta yadda za a kai ga cimma wasu shawarwari cikin makon dake tafe, duka dai da nufin kaiwa ga daukar karin matakai kan kasar ta Rasha game da halin da ake ciki a kasar Ukraine.

Shugaban majalisar Turai Herman Van Rompuy, ya ce yanayin da ake ciki a Ukraine a kwanaki 3 da suka gabata ya yi matukar tsananta, don haka ake bukatar mai da hankali sosai kan kokarin dakatar da zub da jini, da magance kara tsanantar yanayin. Har ila yau ya ce takunkumin da kungiyar EU ta kakabawa Rasha a karshen watan Yulin da ya gabata, ya yi matukar tasiri ga tattalin arzikin ta.

Shi kuwa a nasa bangare, shugaban kwamitin kungiyar EU Jose Barroso, cewa ya yi sanya takunkumin ba shi ne babban burin da aka sanya gaba ba, sai dai ya zama wabiji ne kawai a kakaba shi, domin tilasawa Rashan fahimtar kuskurenta.

Haka zalika Barroso ya jaddada cewa, daukar matakan soji ba za su taba warware matsalar Ukraine ba, don haka ya bukaci Rasha da ta yi hadin gwiwa da kungiyar EU da ma kasar Ukraine a kokarin da ake yi na wanzar da zaman lafiya da lumana a kasar. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China