in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin da kungiyar ASEAN suna da karfin tabbatar da zaman lafiya a yankin tekun kudancin Sin
2014-08-11 11:10:24 cri
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya bayyana a gun taron ministocin harkokin waje na kungiyar ASEAN da aka gudanar a kasar Myanmar a ranar lahadi 10 ga wata cewa, yanzu ana samun zaman lafiya a yankin tekun kudancin kasar Sin, kuma babu matsala kan zirga-zirgar jiragen ruwa ba. Ana ci gaba da raya dangantakar dake tsakanin Sin da kungiyar ASEAN, kuma kasar Sin ta ki amincewa da labaran dake cewa, wai ana shiga hali mai tsanani a yankin tekun kudancin kasar Sin.

Wang Yi ya ce, kasar Sin da kungiyar ASEAN suna da karfin tabbatar da zaman lafiya da na karko a yankin. Ya ce, an cimma daidaito a gun taron ministocin harkokin waje a wannan karo, na ci gaba da aiwatar da sanarwar ayyukan da bangarori daban daban suka yi a yankin tekun kudancin kasar Sin, da kuma yin kokarin cimma ka'idojin ayyuka a yankin cikin hazari.

Ban da wannan kuma, Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin da kungiyar ASEAN sun tattauna batun yankin cikin lumana, abin da ya sa sauran kasashen waje ke iya sa ido a kan batu, amma a ba'a amincewa da su tsoma baki a ciki ba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China