in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Li Keqiang ya tafi lardin Yunnan don jagorancin aikin bada ceto bayan girgizar kasa
2014-08-04 11:00:03 cri

A yau Litinin 4 ga wata da safe ne, firaministan kasar Sin Li Keqiang ya jagoranci tawagar wasu jami'an gwamnati zuwa yankin Ludian na lardin Yunnan da girgizar kasa ta faru don jagorantar aikin bada ceto.

Da karfe 4 da rabi a ranar 3 ga wata, wata girgizar kasa mai karfin maki 6.5 bisa ma'aunin Richter, ta auka a gundumar Ludian dake lardin Yunnan, inda ta haddasa mutuwar mutane da dama.

Ya zuwa karfe 7 na ranar 4 ga wata, mutane 373 sun rasa rayukansu a sakamakon girgizar kasar. A halin yanzu, ana ci gaba da yin kididdiga kan yanayin yankin dake fama da girgizar kasar.

Bisa umurnin da shugaban kasar Sin Xi Jinping da firaministan kasar Li Keqiang suka bayar, hukumomin majalisar gudanarwar kasar da hukumomin yankin da bala'in ya faru sun dauki matakan gudanar da ayyukan bada ceton gaggawa. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China