Mataimakin shugaban kamfanin sadarwa da watsa labarai na kasar(GCIS) Nebo Legaobe, ya ce ana kara samun kasashen nahiyar Afirka da ke shiga manyan gasanni,kuma a shirye suke su rika tallafa kulob-kulob din nahiyar,inda ake fatan za su taka rawar gani fiye da gasar shekarar 2010 da ta gudana a kasar Afirka ta kudu.
Kasashen Najeriya, Ghana, Algeria, Cote d'Ivoire, da Kamaru ne ke wakailtar nahiyar a gasar ta bana da ke gudana a kasar Brazil.(Ibrahim)