in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Najeriya ya daura damarar yaki da 'yan ta'adda
2014-05-30 10:33:24 cri

Shugaban kasar Najeria Goodluck Jonathan ya umurci sojojin kasar da su kaddamar da yaki gadan-gadan da kungiyar Boko Haram domin murkushe barazanar da 'yan ta'addan suke yi.

Shugaban kasar ya bayar da wannan umurnin ne a cikin jawabin da ya yi wa al'ummar kasar na bikin ranar dimokradiyya.

Shugaba Goodluck Jonathan ya jaddada kudurin gwamnati na kare mulkin dimokradiyyar a Najeriya, da kuma tabbatar da hadin kan kasa da samar da zaman lafiya mai dorewa a bangaren siyasa.

Kamar yadda ya ce, gwamnati a shirye take ta yi tattaunawar sulhu da duk wata kungiyar da ke da muradin gaskiya na yin watsi da ta'addanci.

Shugaban kasar ya yi kira a kan 'yan Najeria da su hada kansu, domin samun nasarar yaki da 'yan ta'adda.

Jonathan ya kuma yabawa rundunar sojojojin Najeria a kan sadaukar da kansu da suka yi wajen tunkarar matsalar tsaro, ya kuma bukaci 'yan kasarsa da su jinjina musu maimakon su dinga yin allah wadai da su. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China