in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane uku sun rasu sakamakon harin tashar jirgin kasan yankin Xinjiang
2014-05-01 20:26:33 cri
Rundunar 'yan sandan kasar Sin ta ce wasu mahara su biyu da farar hula daya sun rasa rayukansu, yayin da kuma wasu 79 suka jikkata, sakamakon harin ta'addanci da masu tsattsauran ra'ayi addini suka kaddamar a tashar jirgin kasan Urumqi, dake jihar Xinjiang mai cin gashin kan sa.

Binciken da 'yan sanda suka gudanar ya nuna cewa, daya daga maharan mai shekaru 39 da haihuwa dan asalin gundumar Zayar ne, dake kudancin jiahr na Xinjiang. Kuma a baya ma maharan su biyu, suna da hannu cikin wasu al'amura masu alaka da kaifin kishin addini.

Da karfe 7 da minti goma na almurun jiya Laraba ne dai maharan su biyu, suka tada wani abun fashewa a tashar jirgin kasan dake Urumqi, lamarin da ya haddasa mutuwar su tare da wani mutum guda.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China