in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka ta gargadi 'yan kasarta mazauna Najeriya a lokacin bikin Easter
2014-04-18 15:45:06 cri
Gwamnatin kasar Amurka ta gargadi 'yan kasarta mazauna tarayyar Najeriya da su yi taka-tsantsan a yayin bikin Easter da aka soma tun daga yau ranar Jumma'a zuwa Litinin mai zuwa. Amurka ta bayyana hakan ne bayan harin bom din da yayi sanadiyyar mutuwar mutane da dama tare da jikkata wasu a wata tashar mota dake unguwar Nyanya dake birnin Abuja.

Gwamnatin Najeriya ta bayar da sanawar hutu bikin Easter tun daga yau ranar Jumma'a 18 ga wata har zuwa ranar Litinin 21 ga wata, dalilin haka ne gwamnatin Amurka ta jawo hankalin al'ummarta da suke zaune a kasar dasu kiyaye kansu.

Gwamnatin Amurka ta ci gaba da jan hankalin al'ummarta da su yi kaffa-kaffa a wuraren ibada da sauran wasu wuraren dake dauke da cunkoson jama'a a yayin bikin na Easter.

Murtala, wakilin sashin Hausa na CRI, daga Abuja, Najeriya.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China