in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jihar Kano dake arewacin Najeriya ta maida mabarata jihohinsu
2014-03-21 10:33:43 cri
Gwamnatin jihar Kano dake arewacin tarayyar Najeriya, ta maida mabarata 33 zuwa jihohinsu na asali, a kokarinta na aiwatar da dokar haramta barace-barace a titunan birnin jihar, kamar yadda Darakta-Janar na hukumar Hisbah ta jihar, Dr. Abba Sufi, ya bayyana a kwanan baya.

Dr. Sufi ya ce hukumar ta kuma gurfanar da wani mabaraci a gaban kuliya, saboda karya wannan doka da yayi, ya ci gaba da yawon bararsa.

Ya ce kotun ta yanke wa wannan mabaraci hukuncin dauri na tsawon watanni uku a gidan yari, ko kuma ya biya tarar naira dubu goma.

Sa'annan Darakta-Janar na hukumar ta Hisbah ya kara da cewa, a makon da ya gabata, kwamitin da gwamnatin jihar ta kafa don ganin an kiyaye dokar, ya yi nasarar kama wasu mabarata, wadanda a cewarsa 10 daga cikin su 'yan asalin jihar Jigawa ne, 15 kuma daga jihar Katsina, yayin da 8 suka fito daga jihar Kaduna.

"Dukkansu yanzu haka suna hanyar komawa jihohinsu, za mu damka su a hannun sakatarorin gwamnatocin jihohinsu", in ji Sufi.

Haka kuma ya ce akwai masu tabin hankali guda bakwai da aka kama, wadanda a yanzu haka suke a asibitin mahaukata na Dorayi, domin ba su kulawa da duba lafiyarsu.(Murtala)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China