in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen kasar Sin ya gana da shugaban kungiya mai adawa da gwamnatin Syria
2014-04-16 21:00:22 cri
Yau Laraba 16 ga wata, ministan harkokin waje na Sin Wang Yi ya gana da shugaban jam'iyyar kungiyar adawa da gwamnatin Syria mai suna "Kawancen 'yan adawa da gwamnati da masu juyin juya hali", Ahmad al-Jarba da 'yan rakiyarsa, wadanda suka zo nan birnin Beijing bisa goron gayyatar cibiyar diplomasiyyar jama'a ta Sin.

A lokacin ganarwa su Mr Wang ya ce, yanzu ana cikin yanayin tangal-tangal a Syria don haka Kamata ya yi bangarori daban daban na Syria su dora muhimmanci kan al'umma da kasar, su tsagaita bude wuta tun da wuri.

Ministan yayi kira da su sa kaimi ga yunkurin siyasa mai dorewa, a kokarin tabbatar da kudurin kwamitin sulhu na MDD mai lamba 2139 a duk fannoni, ta yadda za a cimma burin daidaita matsalar Syria a siyasance tun da wuri.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China