in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Senegal da Mali za su karfafa dangantakarsu ta fuskar tsaro
2014-04-16 14:42:34 cri

Shugaban kasar Senegal Macky Sall da takwaransa na kasar Mali Ibrahim Boubacar Keita sun dauki niyyar karfafa dangantakarsu ta fuskar tsaro, musammun ma wajen yaki manyan laifuffukan kasa da kasa, a cewar wata sanarwar da ta biyo bayan karshen ziyarar kwanaki biyu da shugaban kasar Mali ya kai birnin Dakar.

Dangantakar tsaron za ta tabo musammun ma batun yaki da ta'addanci, ta hanyar gudanar da sintirin hadin gwiwa tsakanin jami'an tsaron kasashen biyu, in ji wannan sanarwa. A gaban tashe-tashen hankali da yake-yake dake faruwa a wasu yankunan nahiyar Afrika, da karuwar ayyukan ta'addanci a yankin Sahel, kasashen Mali da Senegal sun bayyana damuwarsu ta hanyar yin kira ga zaman lafiya, zaman karko da hadin kan al'ummar kasashen nahiyar Afrika.

A wasu fannoni, in ji sanarwar, shugabannin biyu sun jaddada niyyar matuka wajen bunkasa noma da kuma ingiza kasashen biyu zuwa matsayin koli. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China