in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zimbabwe ta tsaurara matakan sanya ido kan harkokin kudi
2014-04-10 10:44:33 cri

A kasar Zimbabwe, hukumar haraji ta kasar ta gabatar da shirin tsaurara matakan sanya ido kan harkokin kudi a kasar domin kawar da matsalar ficewar makudan kudade daga kasar.

Babban jami'in hukumar haraji ta kasar Zimbabwe, mista Geshorn Pasi ya bayyana cewa, kasar tana fama da matsalar ficewar kudade masu tarin yawa. Kasar tana amfani da kudaden kasashe waje a halin yanzu, dalar Amurka ita ce aka fi amfani da ita a cikin kasar, kuma a matsayin kudin misali da na hada hada.

Mista Pasi ya shaida wa wani kwamitin 'yan majalisu a ranar Talata cewa, hukumarsa ta gabatar da wasu matakai ga gwamnatin kasar domin magance matsalar ficewar kudade. A halin yanzu, mutumin kasar Zimbabwe guda na iyar fita daga kasar da dalar Amurka dubu goma a ko wace tafiya ba tare da an takaita yawan balaguron ba, domin haka ne kudade da dama suke fita daga kasar, in ji jami'in. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China