in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
za'a tsugunar da 'yan gudun hijirar dake Botswana a wata kasa ta daban
2014-04-09 10:20:30 cri

Wani jami'in hukumar kula da 'yan gudun hijira ta majalisar dinkin duniya (HCR) ya tabbatar a ranar Talata cewa, ana binciken wasu hanyoyi domin sake tsugunar da wasu 'yan gudun hijira da a yanzu haka suke zaune a cikin sansanin 'yan gudun hijira na Dukwi dake kasar Botswana, bayan boren baya bayan nan na wadannan 'yan gudun hijira kan tabarbarwar halin zaman rayuwarsu a wannan wuri.

A cewar HCR, kasar Botswana ta karbi 'yan gudun hijira kimanin dubu uku da kuma masu neman mafaka da yawancinsu suka fito daga kasashen Somaliya, Namibiya da Zimbabwe.

Suna zaune a sansanin na Dukwi, inda gwamnatin kasar ta Boswana ta dauki nauyin ba su hidimar ba da ilimi da kiwon lafiya. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China