in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Sin ya isa birnin Berlin don fara ziyarar aiki a Jamus
2014-03-28 19:39:50 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping a yau Jumma'a 28 ga wata ya isa birnin Berlin na kasar Jamus domin fara ziyarar aiki a zangon shi na uku na ziyarar da yanzu haka yake yi a kasashen Turai.

Wannan ziyarar ita ce ta farko da wani Shugaban kasar Sin ya kai Jamus a cikin shekaru 8. A lokacin ziyarar, Shugabannin kasashen biyu za su fitar da tsarin da dangantakar kasashensu za ta bi nan da shekaru 5 zuwa 10 da zai kawo dabarun ci gaba da hangen nesa.

Lokacin da ya isa Berlin, Shugaban Xi ya ce, hadin gwiwa tsakanin Sin da Jamus ta samu nasarorin masu dimbin yawa tun lokacin da kasashen biyu suka kulla huldar diplomasiyya shekaru 40 da suka gabata, sannan kuma kasashen 2 na da ra'ayi daya a kan fadada dangantakarsu da bullo da sabbin hanyoyin hadin gwiwa.

A cikin jawabinsa, Shugaba Xi ya ce, yana sa ido wajen yin aiki da shugabannin Jamus domin su bullo da hanyoyin inganta ci gaba tsakanin kasashen biyu ganin cewa, an tuntubi mutane daga bangarori daban daban na kasar Jamus a kan hadin gwiwa da kulla abota da kuma daukaka dabarun ci gaba na kasashen biyu zuwa wani sabon mataki.(Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China