in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban sojojin Masar ya sanar da takararsa a zaben shugaban kasar
2014-03-27 15:06:47 cri

Shugaban rundunar sojojin kasar Masar Abdel-Fattah al-Sisi ya sanar a ranar Laraba da takararsa a zaben shugaban kasar mai zuwa, bayanin da mutanen kasar suka jima suna jira tun bayan kifar da gwamnatin tsohon shugaban kasar a cikin watan Yulin shekarar 2013.

Wannan ita ce bayyanata ta karshe a gabanku a cikin kayan soja, in ji mista Sisi a cikin wata sanarwa ta kafar talabijin.

Na dauki niyyar yin murabus daga mukamina na shugaban rundunar sojojin kasar da na ministan tsaro, in ji jagoran kifar da gwamnatin Mohamed Morsi.

Ina sanar da ku da sahihiyar takarata a zaben shugaban kasa, in ji mista Sisi, tare da bayyana cewa, ya sanya kayan soja domin kasar Masar kuma zai fitar da shi domin kasar Masar. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China