in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar Hisba ta jihar Kano ta lalata kwalaben giya dubu 200 a shekara ta 2013
2014-01-24 16:12:53 cri

Kwanan baya, hukumar Hisba ta jihar Kanon Najeriya ta bayyana cewa, a cikin shekarar da ta gabata wato shekara ta 2013, ta lalata ire-iren giya da yawansu ya zarce kwalabe dubu 200, wadanda darajarsu ta kai miliyoyin Naira.

Babban darektan hukumar Hisba ta jihar Kano Dr. Abba Sufi ya tabbatar da hakan ne a cikin wata zantawa da yayi da kamfanin dillancin labaran kasar ta Najeriya wato NAN a Kano.

Dr. Abba ya ce, dukkanin giyan an kwace su ne daga hannun dillalai gami da sauran jama'a a cikin kananan hukumomi 44 na jihar ta Kano.

A cewar Dr Abba, shekara ta 2013, muhimmiyar shekara ce ga hukumar Hisba saboda ta lalata kwalaben giya da dama. Ya ce, bisa dokar da aka kafa a shekara ta 2001, dukkan ayyukan da suka shafi shan giya, da saye da sayar da ita, da samar da ita, da kuma yin jigilarta,an haramta su a jihar Kano.

Har wa yau kuma, Dr. Abba Sufi ya ce, hukumar Hisba ta cafke mata masu yin karuwanci guda 66 a cikin makwanni biyu da suka gabata a Kano.

Game da harkar bara a kan titunan Kano kuwa, Dr. Abba ya ce, gwamnatin jihar ta kafa wani kwamiti mai mutane 100, a wani kokari na karfafa dokar hana bara a kan tituna a jihar.

Murtala, wakilin sashin Hausa na CRI, daga Abuja, Najeriya.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China