in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun wanzar da zaman lafiya na Sin sun tashi zuwa Liberia
2014-03-20 10:21:21 cri

A ranar Laraba da dare, agogon kasar Sin ne rukuni na 16 na dakarun wanzar da zaman lafiya na kasar Sin suka tashi zuwa kasar Liberia.

Tawaga ta farko mai kunshe da dakaru 558 daga bataliyar soja da ke birnin Beijing ta tashi ne daga filin tashi da saukar jiragen sama na kasa da kasa da ke nan birnin Beijing. Yayin da ake sa ran tashin kashi na biyu na tawagar a ranar 29 ga watan Maris.

Tawagar wadda za ta shafe watanni 8 tana aiki kamar yadda MDD ta bukata, za ta gudanar da ayyukan da suka shafi sufuri, aikin injiniya, da kuma lafiya.

A watan Disamban shekarar 2003 ne kasar Sin ta fara tura dakarun wanzar da zaman lafiya zuwa kasar ta Liberia. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China