in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
EU ta saka wa wasu jami'ai takunkumi
2014-03-18 12:54:17 cri

Kungiyar tarayyar Turai EU ta sanya wa wasu mutane 21 da ake ganin suna da hannu wajen shirya zaben raba gardamar da aka yi a yankin Crimea. Matakin da kungiyar ta ce ya haifar da barazana ga 'yancin kasar Ukraine.

Kungiyar ta bayyana hakan ne cikin wata sanarwa bayan kammala taron ministocin harkokin wajenta a ranar Litinin.

Kungiyar ta kuma yi kira ga kasar Rasha da ta dauki matakan da suka dace, don kashe wutar fitinar da ke faruwa, kana ta fara tattaunawa kai tsaye da gwamnatin Ukraine. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China