in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana ci gaba da fuskantar tashin hankali tsakanin gwamnatin Mozambique da 'yan adawa
2014-03-06 10:02:40 cri

Babbar jam'iyyar adawa ta Renamo da ke kasar Mozambique, ta koka kan hare-haren da dakarun gwamnati ke kai musu a tsakiyar kasar, yayin da sassan biyu ke bayyana kudurinsu a farkon wannan mako na tsagaida bude wuta.

Kakakin jagaron Renamo, Antonio Muchanga, ya bayyana cewa, jam'iyyarsa ta yi mamakin yadda dakarun gwamnatin dauke da muggan makamai suka durfafi sansanin jam'iyyar a daren ranar Talata.

Sai dai kakakin tawagar gwamnatin Frelimo Jose Pacheco, a tattaunawar da suka yi da Renamo, ya mayar da martanin cewa, dakarun gwamnatin suna farautar wadanda ake zargi da kai hare-hare ne kan motar soja a ranar Litinin, harin da ake zargin Renamon da kaiwa.

A daya bangaren kuma, tawagogin biyu sun bayyana kudurinsu na kawo karshen fadace-fadacen da suka faru a ranar Litinin bayan zaman sasantawar.

Pacheco ya tabbatar da cewa, an samar da matakan samar da zaman lafiya, ko da yake ba yanzu za a bayyana su ba.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China