in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fidda sabon tsarin tallafawa miliyoyin al'ummar dake yankunan Sahel
2014-02-04 16:21:06 cri
MDD tare da gamayyar kungiyoyin jin kai na kasa da kasa, sun kaddamar da wani sabon tsari, wanda zai shafi shekaru 3 yana taimakawa mutane miliyoyi 2 dake yankin Sahel a nahiyar Afirka, fita daga kangin yunwa dake yi wa yankin barazana.

A cewar kakakin MDD Martin Nesirky, za a bukaci taimakon kudi daga kasashen duniya, da yawansu zai kai dalar Amurka miliyan dubu biyu, domin baiwa al'ummun yankin na Sahel tallafin kandagarki daga yunwa, da karancin tsaro kamar yadda shugabar sashen kula da ayyukan jin kai na majalissar Valerie Amos ta bayyana yayin kaddamar da sabon shirin ranar Litinin a birnin Rome na kasar Italiya.

A nasa tsokaci babban daraktan hukumar aikin noma ta MDD Jose Graziano da Silva, cewa ya yi cikin manufofin sabon shirin akwai samar da nagartattun kayan noma da za su inganta yabanyar da manoman yankin za su shuka a kakar bana.

Sabon shirin na wannan karo dai ya kunshi tanaji na musamman ga kasashen Chadi, da Burkina Faso, da Kamaru da Gambia. Sauran kasashen sun hada da Mali, da Mauritaniya, da Nijar, da Senegal da kuma Najeria. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China