in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar adawa ta Syria ta dakatar da kudurinta na halartar taron Geneva
2014-01-20 21:03:09 cri

Babbar kungiyar adawa ta Syria NCSROF ta sanar a ranar Litinin 20 ga wata cewa, ba za ta halarci taron Geneva na 2 dangane da batun Syria ba, sai dai idan MDD ta soke gayyatar da ta ba kasar Iran, ko kuma idan Iran ta amince da sanarwar taron Geneva na farko.

A cikin sanarwar da Louay Safi, kakakin kungiyar NCSROF ya fitar ya ce kungiyar za ta shirya wani taron manema labaru musamman ma a kan batun.

Kafin haka, kunigyar NCSROF ta sanar a Istanbul na kasar Turkiya a ranar Asabar 18 ga wata cewa, za ta halarci taron Geneva na 2 da zai gudana a ranar 22 ga wata. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China