in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jean Loius Robinson ya ki amincewa da kayen da ya sha a zaben shugabancin kasar Madagascar
2014-01-18 16:38:49 cri
Dan takarar da ya fafata da wanda ya lashe zaben shugaban kasar Madagascar da aka yi a ranar 20 ga watan Disamba wato Jean Loius Robinson, ya ki amincewa da sakamakon da kotun zaben kasar ta musamman (CES) ta sanar a hukumance.

Robinson ya nuna wa manema labarai wasu ambulan kunshe da wasu takardun sakamakon zaben da aka like daga tashoshin zabe da za a aika wa hukumar zaben kasar, matakin da dan takarar ya ce abu ne da ba za a lamunta ba.

Ya ce magoya bayansa za su fito kan tituna su yi zanga–zanga, amma za su tsaya ne wurin da za su yi taro, domin su nemi 'yancinsu.

Shugaban kotun musamman mai kula da harkokin zaben kasar ce Rakotozafy Francois ya bayyana sakamakon zaben a safiyar ranar Jumma'a, inda ya nuna cewa, Hery Rajaonarimampianina ne aka zaba a matsayin shugaban kasar ta Madagascar ta kashi 53.49 cikin 100 na kuri'un da aka kada, yayin da Jean Robinson ya samu kashi 46.51 cikin 100. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China