Shugabar hukumar zaben kasar mai zaman kanta(CENI-T) Atallah Beatrice, ta shaida wa wakilin kamfanin dillancin labarai na Xinhua yayin da take duba yadda zaben ke gudana a rumfar zabe ta Alarobia cewa, an fara zaben a baki dayan rumfunan zaben kasar 20,001 yadda ya kamata.
Ta bayyana cewa, tun daga karfe 5 na safe agogon wurin wasu rumfunan zabe suka bude wato sa'a guda kafin lokacin bude rumfunan a hukumance.
A wannan rana ne kuma ake gudanar da zabukan 'yan majalisun dokokin kasar. (Ibrahim)