in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 71 suka mutu sakamakon cutar kwalara a arewacin Nijeriya
2014-01-11 20:27:51 cri
Rahotanni daga jihar Kano a arewacin Tarayyar Nigeriya na nuna cewa akalla mutane 71 ya zuwa yanzu suka mutu sakamakon cutar kwalara ,kamar yadda wani jami'i ya tabbatar ma kamfanin dillanci labarai na Xinhua.

Annobar ta fada wassu unguwanni a sassa daban daban na jihar ,kamar yadda Abdulsalam Nasidi Darektan shirye shirye na sashin kula da yaduwar cututtuka na ma'aikatar kiwon lafiya na gwamnatin tarayyar kasar ya shaida ma manema labarai inda yace an samu rahoton wadanda suka kamu da cutar su 2,165 a wadannan wurare a jihar cikin watannin biyu da suka gabata.

Gwamnatin tarayya inji shi ta rigaya ta aike da wata tawaga zuwa jihar domin taimakawa magance wannan cuta sannan suka mika taimakon magungunan domin hana yaduwarta.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China