in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi kidayar kuri'un zaben shugaban kasar Madagascar a hankali
2013-10-27 17:28:50 cri
An yi zaben shugaba a kasar Madagascar dake kudu maso gabashin nahiyar Afirka a ranar 25 ga wata, wannan ne karo na farko da aka yi zaben shugaban kasar a shekaru 5 da suka gabata. A halin yanzu rashin ingantattun hanyoyin sufuri a yankunan kasar da dama ya sa ana tattara kuri'un zabe da kidaya su sannun a hankali.

Ya zuwa karfe 6 na daren ranar 26 ga wata, hukumar zaben kasar ta gabatar da sakamakon tasoshin jefa kuri'u guda 366, duk da cewa jimilar tasoshin jefa kuri'u a kasar ta kai 20,001. Babban sakataren hukumar Jean Victor Rasolonjatovo ya ce, ana bukatar kowace tashar jefa kuri'u da ta aika sakamakon kidaya kuri'unta zuwa hukumar zaben kasar, amma matsalar ita ce wasu yankuna ba su da hanyoyin sufuri masu kyau , shi ya sanya ana bukatar kwanaki 7 zuwa 10 don tattara da kidayar dukkan kuri'un zaben.

Bisa sakamakon kidaya kuri'un da aka samu a halin yanzu, an ce, dan takara Jean Louis Robinson da tsohon shugaban kasar Marc Ravalomanana ke nuna goyon baya da tsohon ministan kudi na kasar Hery Rajaonarimampianina suke a sahun gaba. Amma manazarta sun nuna cewa, ganin akwai 'yan takara da dama, abin zai yi wuya a samu wani dan takara da zai samu kuri'u fiye da rabin yawan kuri'un zaben a zagayen farko, don haka akwai yiwuwar zagaye na biyu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China