in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Halayyar tawaliwu ta Nelson Mandela ta burge ni kwarai da gaske, in ji Ban Ki-moon
2013-12-10 15:16:22 cri

Ran 9 ga wata, babban magatakardar MDD Ban Ki-moon ya bayyana a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu cewa, rasuwar tsohon shugaban kasar Afirka ta Kudu Nelson Mandela ta haifar da rashin wani jarumi na duniya baki daya. Mr. Ban ya kara da cewa halayyar Mandela ta burge shi kwarai da gaske, ta kuma ba shi kwarin gwiwa matuka.

Mr. Ban na daya daga cikin rukunin farko na manyan jami'an kasa da kasa da suka isa kasar Afirka ta Kudu, domin halartar bukukuwan jana'izar da gwamnatin Afirka ta Kudu ta shriya. Yayin ganawarsa da wakilan kafofin watsa labarai, Mr. Ban ya ce alal hakika rashin Mandela wani abun takaici ne ga daukacin duniya. Ya ce Nelson Mandela mutum ne da ya ba da gaskiya ga ayyukan tabbatar da adalci tsakanin 'yan dan Adam, da kuma kare hakkin dan Adam.

Har yanzu dai jama'ar kasar Afirka ta Kudu, da al'ummunomin kasa da kasa, su na ci gaba da nuna jimami da bakin ciki don gane da rashin wannan jarumi.

Yayin da Mr. Ban Ki-moon ke tunawa da ganawarsa tare da Mandela a shekarar 2009, ya bayyana cewa, halayyar tawaliwu ta tsohon shugaban ta burge shi kwarai, har ya zuwa yanzu kuma yana koyi da shi.

A Ranar 9 ga wata da yamma ne dai Mr. Ban da wasu jami'an MDD suka ziyarci asusun Nelson Mandela, da kuma wasu abubuwan tarihi dake bayyana zaman rayuwar Nelson Mandela. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China