in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugaban kasar Sin ya je ofishin jakadancin Afirka ta Kudu don mika ta'aziyya bisa ga rasuwar Mandela
2013-12-06 20:52:02 cri

Mataimakin shugaban kasar Sin Li Yuanchao ya je ofishin jakadancin Afirka ta Kudu dake nan birnin Beijing a yau Jumma'a 6 ga wata don mika ta'aziyya bisa ga rasuwar tsohon shugaban kasar Nelson Mandela.

Li Yuanchao ya nuna alhini a gaban mutum-mutumin na Mandela, inda ya rubuta sakon ta'aziyya a littafin da aka kebe don mika sakon ta'aziyya. Kana Li Yuanchao ya bayyana cewa, Mandela ya yi kokarin kiran samun daidaici da sulhuntawa a tsakanin kabilu daban daban na kasar. Ya kasance jarumi a cikin zuciyar jama'ar kasar Afirka ta Kudu, kana kasa da kasa sun nuna yabo gare shi. A madadin gwamnatin kasar Sin da jama'arta, Li Yuanchao ya mika ta'aziyya bisa ga rasuwar Mandela. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China