in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A kalla mutane 12 suka mutu, 5 suka jikkata a fada tsakanin kungiyar 'yan tawaye a arewacin Kenya.
2013-12-05 11:11:31 cri
A ranar Laraban nan 4 ga wata kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua ya ba mu labarin cewa, a kalla mutane 12 ne suka rasa rayukan su 5 kuma suka jikkata a yankin Marsabit dake arewacin kasar Kenya sakamakon wani arangama tsakanin kungiyoyin 'yan tawaye guda biyu.

Dubban mazauna galibi mata, yara da tsofaffi sun kaurace ma gidajen su dake bakin iyaka sakamakon jita jitar da ake yadawa na daukar fansa.

Kwamandan rundunar 'yan sandan yankin Moyale, Nehemiah Lagat ya ce an riga an tura daruruwan jami'an 'yan sanda a wannan yanki domin shawo kan al'amarin.

Wannan kashe kashe dai ya zo ne kwanaki biyu bayan da wani ma'aikacin wannan yanki na Moyale aka mashi yankan rago, aka kuma kashe wani mai gadin gida a unguwar Karare da ke Marsabit, abin da ya sa daruruwan mazauna suka tsere daga gidajen su saboda gudun ramuwar gayya.

Fiye da mutane 30 aka kashe a cikin shekara daya a wannan yankin sakamakon tashe tashen hankula na kabilanci da ake fuskanta tsakanin kabilun Borana, Gabra da Rendile. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China