in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jam'iyyar PDP ta Nijeriya na fatan koyon darussan cikakken zama karo na uku na kwamitin tsakiyar JKS na 18
2013-11-27 20:06:08 cri

Alhaji Bamanga Tukur, shugaban jam'iyyar PDP dake rike da mulkin kasar Nijeriya, wanda yake ziyara a nan kasar Sin, ya ce, jerin matakan yin gyare-gyaren da aka gabatar a gun cikakken zama karo na uku na kwamitin tsakiyar JKS na 18 sun burge shi .

A hirarsa da wakilinmu a yau Laraba 27 ga wata a nan birnin Beijing, Alhaji Bamanga Tukur ya bayyana fatansa na cewa, za a dauki darasi daga wadannan matakai, a kokarin taimakawa Nijeriya wajen yin kwaskwarima.

Dangane da yin kwaskwarima kan yaki da cin hanci da rashawa, Alhaji Bamanga Tukur ya ce, yaki da cin hanci da rashawa da gwamnatin Sin take yi, babban dalili ne na samun bunkasuwar tattalin arzikin kasar cikin sauri. Don haka shi ma yana fatan jam'iyyar dake rike da mulkin kasar Nijeriya PDP za ta bi hanyar da JKS take bi don horar da membobinta, tare da daukar matakan yin bincike da kansu ko kuma yin binciken juna, a kokarin tabbatar da kyakkyawar dabi'ar jam'iyyar, da sa kaimi ga bunkasuwar kasar baki daya. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China