in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi kira da a kara daukar matakan habaka masana'antu a Afirka
2013-11-23 16:14:35 cri
Babban sakatare a ma'aikatar cinikayya, masana'antu da harkokin zuba jari a tarayyar Najeriya Dauda Kigbu, ya yi kira ga daukacin masu ruwa da tsaki da su dukufa wajen zakulo hanyoyin bunkasa masana'antu a nahiyar Afirka.

Kigbu, wanda ya bayyana hakan cikin sakon da daraktan tsare-tare, da kididdiga na ma'aikatar ya karanta a madadinsa, yayin bikin bude taro na 23 na Ranar Bunkasa Masana'antun Nahiyar da aka gudanar a babban birnin tarayyar Najeriya Abuja, ya kara da cewa wannan taro wata dama ce ga mahalartansa, ta hada karfi da karfe wajen tunkarar matsaloli, da kalubalen da sashen masana'antun nahiyar ke fuskanta.

Babban sakataren ya kuma bayyana irin gudummawar da masana'antu ke baiwa ci gaban al'umma, ciki hadda batun samar da ayyukan yi, da bunkasa tattalin arziki. Ya ce har yanzu Najeriya, da ma nahiyar Afirka, ba su ci cikakkiyar gajiyar dinbin al'ummar dake akwai a nahiyar ba, duk da mai da hankali da ake yi ga sassan tattalin arziki masu alaka da albarkatun mai da iskar gas a kasashe da dama dake nahiyar.

Bisa la'akari da hakan, Kigbu ke ganin lokaci ya yi da za a dauki dukkanin matakan da suka wajaba, don fadada cin gajiyar ragowar sassan tattalin arziki, da zasu amfani nahiyar ta Afirka. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China