in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin tana son kara hadin gwiwa a tsakaninta da kasashe masu amfani da harshen Portugese
2013-11-04 21:21:57 cri
A Yau Litinin 4 ga wata a yankin Macau dake kasar Sin, mataimakin firaministan kasar Sin Wang Yang ya gana da shugabannin kasashe masu amfani da harshen Portugese dake halartar taron ministoci karo na 4 na dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da kasashe masu amfani da harshen Portugese, inda yake fatan za a yi amfani da wannan dandalin hadin gwiwa a tsakanin gwamnatoci don inganta hadin gwiwarsu.

Yayin da yake ganawa da firaministan gwamnatin wucin gadi ta kasar Guinea-Bissau Rui Duarte de Barros, Wang Yang ya bayyana cewa, Sin tana kokarin raya dangantakar hadin gwiwa a tsakanin Sin da kasar Guinea-Bissau, kana za ta ci gaba da nuna goyon baya ga Guinea-Bissau wajen samun zaman lafiya da bunkasuwa, kuma yana fatan kasashen biyu za su kara yin hadin gwiwa a fannonin aikin noma, kamun kifi, ma'adinai, albarkatun ma'aikata da dai sauransu.

A nasa bangare, Barros ya bayyana cewa, kasarsa tana son zurfafa dangantakar dake tsakaninta da kasar Sin, da kara yin hadin gwiwa a fannoni daban daban, ta yadda za a raya kasar yadda ya kamata.

Za a gudanar taron ministoci karo na 4 na dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da kasashe masu amfani da harshen Portugese a ranar 5 ga wata a yankin Macau. Ana sa ran Wang Yang zai halarci bikin bude taron tare da yin jawabi. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China