in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi garkuwa da firaministan kasar Libya
2013-10-10 15:31:40 cri
Bisa bayanin da gidan telebijin Al-Arabiya ya bayar, an ce, a ranar 10 ga wata da sanyin safiya, an yi garkuwa da firaministan kasar Libya Ali Zidan a birnin Tripoli hedkwatar kasar Libya, kuma har yanzu ba a san inda yake ba.

Ban da wannan kuma, kakakin Ali Zidan ya tabbatar da wannan labari ga shafin Internet na CNN na Amurka.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, dakarun dauke da makamai da ba a san su wane ne ba, sun yi awon gaba da Zidan a otel da yake zaune, kuma cikin mutanen da aka sace tare da shi, har da wasu na hannun damarsa. Har zuwa yanzu, dai babu wata kungiyar da ta sanar da daukar alhakin wannan lamari.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China