in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wani mai gabatar da kara na bangaren soji na Libya ya rasu sakamakon kisan gillar da aka yi masa
2013-08-30 17:08:50 cri
A ranar 29 Alhamis ne, wani jami'in hukumar tsaron kasar Libya ya bayyana cewa, a wannan rana, an kai harin boma-boman da aka dasa cikin mota a birnin Benghazi da ke yankin gabashin kasar, lamarin da ya haddasa mutuwar wani mai gabatar da kara na bangaren soji na Libya.

Kakakin hukumar tsaro cikin hadin gwiwa ta birnin Benghazi ya bayyana cewa, an kai hari ga mai gabatar da kara na bangaren soji na Libya mai suna Yusuf Alas Fuer, harin da ya yi sanadiyyar mutuwarsa.

Alas Fuer ya taba shiga aikin yanke hukunci ga manyan jami'an tsohon mulkin Gaddafi da dama na kasar.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China